Isa ga babban shafi
Najeriya

Rundunar Soji ta gargadi Jami’anta kan jita-jitan juyin mulki

Rundunar Sojin Najeriya ta gargadi sojoji da su kaucewa sanya hannun su cikin harkokin siyasa, ko kuma su gamu da fushin hukuma.

Babban hafsan Sojin Najeriya Janar Tukur Yusuf Buratai
Babban hafsan Sojin Najeriya Janar Tukur Yusuf Buratai AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Mai Magana da yawun rundunar Janar Sani Usman Kukasheka ya ce shugaban sojin Janar Tukur Burutai ya samu bayanan da ke nuna masa cewar wasu ‘yan siyasa sun tuntubi wasu kananan sojojin ba tare da cikaken bayani a kai ba

Janar Kukasheka ya ce duk sojan da ke sha’awar sanya hannu cikin siyasa na iya aje aikin sa domin tsunduma cikin siyasar.

Majiyoyin tsaro sun shaida cewa an sanar da babban hafsan sojin kasar da mukadashin shugaban kasa Yemi Osibanjo cewa ana shiryawa gwamnati manakisa, dalilan da ya sa suka alkawarta shawo kan lamarin.

An shafe shekaru 18 ana tafiyar da mulkin demokrudiya a Najeriya tun bayan karbe iko daga sojoji a shekarar 1999 cikin kwanciyar hankali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.