Isa ga babban shafi
Najeriya

An rantsar da Amina Muhammed

An rantsar da tsohuwar ministan muhallin Najeriya Amina Muhammed a matsayin mataimakiyar Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York.

Amina Mohammed a lokacin rantsuwar kama aiki a Majalisar Dinkin Duniya.
Amina Mohammed a lokacin rantsuwar kama aiki a Majalisar Dinkin Duniya. UN Photo/Mark Garten
Talla

Sakatare Janar Antonio Guterres ya rantsar da ita, bayan nadin da ya mata a watan jiya.

Amina Muhammed ita ce mace ta biyu da za ta rike wannan mukamin bayan Asha-Rose Migiro ‘yar kasar Tanzania da ta rike mukamin a karkashin Ban Ki Moon tsakanin 2007 zuwa 2012., ta kuma maye gurbin Jan Eliasson na kasar Sweden karkashin shugabancin Ban Ki-Moon.

Ana ganin Amina za ta taka muhinmiyyar rawa na kawo sauyi da zai kunshi daidaito musanman ‘yancin mata.

Amina Muhammed ta rike mukamin ministar Muhalli a Najeriya kafin zama mataimakiyar sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniya.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.