Tattaunawa da Ra'ayin masu saurare
Ra'ayoyi kan Hukumar da gwamnatin Najeriya ta kafa kan hauhawar farashin kayan masarufi
Wallafawa ranar:
Kunna - 14:58
Shirin ra'ayoyin masu sauraro ya tattauna ne kan hukumar da majalisar zartarwar tarayyar Najeriya ta kafa, domin sa ido da kuma kawo karshen hauhawar kayayyakin masarufi a kasar. A rana Larabar da ta gabata mataimakin shugaban kasar Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, ya jagoranci zaman majalisar zartawar da ta amince da matakin.