Ranar 1 ga watan Oktoba, ta kasance mai girma a tarihin Nigeria, kasancewa a ranar kasar ta samu ‘yancin mulkin kai daga kasar Ingila, inda a gobe ake cika shekaru 56 da samun ‘yancin.
Daga cikin wadanda suka yi gwagwarmayar samar wa kasar wannan ‘yanci, akwai Alhaji Abubakar Tafawa Balewa, wanda ya rike mukamin Firaministan farko a kasar.
Shekaru kusan 50 bayan kisan gillar da aka yi wa marigayi Tafawa Balewa, ko yaya yanayin rayuwar iyalan da ya bari ?
Muhammad Ibrahim Bauchi ya zanta da daya daga cikin ‘ya’yansa wacce yanzu ke rike da mukamin Shugabar Hukumar Yaki da Jahilci a jihar Bauchi, Hajia Yelwa Abubakar Tafawa Balewa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu