Isa ga babban shafi
Najeriya-Boko Haram

Boko Haram ta yi sanadin raba yara miliyan daya da gidajensu

Majalisar Dinkin Duniya ta ce hare-haren kungiyar Boko haram yayi sanadin raba kananan yara kimanin miliyan daya a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Wasu kananan yara da rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu
Talla

Rahoton Majalisar Dinkin Duniyar ya kara da cewa, a kalla malaman makarantu 19,000 suka tsere daga arewa maso gabashin Najeriya, yayinda 611 suka rasa rayukansu, sakamakon tashin hankalin da kungiyar Boko Haram ta haddasa daga shekarar 2009 zuwa 2015.

Wani jami’i a sashin yada labaran Majalisar Dinkin Duniyar, Oluseyi Soromekun, ya tabbatar da wannan rahoto wanda za’a wallafa shi a ranar Litinin mai zuwa, a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.

A cewar rahoton hare-haren kungiyar Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar, ya rusa a kalla makarantu 910, yayinda kuma wasu 1,500 suka rufe bisa tilas.

Hakan ya sa Majalisar Dinkin Duniya bayyana bukatar maida hankali wajen farfado da ilimi a yankin cikin gaggawa, domin a tafi da yankin wajen cimma muradin bunkasa ilimi a nahiyar Afirka nan da shekara ta 2089.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.