Najeriya
Buhari ya jinjina wa shugaban Facebook
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya jinjina wa shugaban kamfanin sadarwa na facebook, Mark Zuckerberg saboda yadda ya zaburar da matasan kasar a fannin fasahar sadarwa.
Wallafawa ranar:
Talla
Buhari ya yi jinjinar ne bayan ya gana da Zuckerberg a fadarsa da ke birnin Abuja a jiya jumma’a.
A ranar Talatar da ta gabata ne, Zuckerberg mai shekaru 32 kuma na biyar wajen arziki a duk fadin duniya, ya ziyarci birnin Legas, inda ya gana da matasa masu shawa’ar bunkasa ilimin sarrafa kwamfuta.
Zuckerberg ya ce, matasan Najeriya nada basira a fannin fasahar sadarwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu