Najeriya
Bam ya hallaka mutane 5 a Biu
Rundunar sojin Najeriya ta ce mutane biyar ne suka rasa rayukansu sakamakon fashewar wani abu da aka ce bam ne, a wajen garin Biu na jihar Borno mai fama da ayyukan Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin Rundunar Sojin Kanar Sani Usman ya ce Bam din ya tashi ne a kan titin Biu zuwa Damboa lokacin da wani babur mai kafa Uku ya take shi bisa kuskure.
Daga cikin wadanda suka rasa rayukansu har da wata mata da kuma jinjirinta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu