Isa ga babban shafi
Najeriya

Yau ne Fulani za su fice daga kudancin Najeriya

Yau ne wa’adin da matasan Igbo suka bai wa Fulani makiyaya da ke kudu maso gabashin Najeriya da su fice daga yankin ke cika, ko kuma su yi amfani da karfi wajen korar su.

Ana zargin Fulani makiyaya da kaddamar da harin Enugu, wanda ya kashe sama da mutane 40 a ranar Litinin.
Ana zargin Fulani makiyaya da kaddamar da harin Enugu, wanda ya kashe sama da mutane 40 a ranar Litinin. screammie.com
Talla

Matasan sun bayar da wa'adin ne karkashin kungiyar Ohanaeze ta kabilar Igbo kuma daukan matakin ya biyo bayan zargin Fulanin da hallaka 'yan kabilar Igbo sama da 40 a jihar Enugu, kamar yadda shuagban matasan Mazi Obinna Achuoye ya bayyana.

Shugabannin Fulani sun musanta zargin cewa, Fulani makiyaya ne suka kaddamar da harin.

Bayan wani taro da suka yi a jihar Kaduna, gwamnonin yankin Arewacin kasar sun bayyana bacin ransu kan yadda ake cin zarafin Fulanin, maimakon hukunta wadanda suka aikata laifi.

Gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima ya yi Allah-wadai kan yadda ake alakanta rikicin Fulani da siyasa a Najeriya.

01:09

Kashim Shettima kan rikicin Fulani

Shugabannin kabilar Igbo na cewa, rikicin Fulani ya tirsasa wa mata da kananan yara ficewa daga gidajensu yayin da rahotanni ke cewa, tuni wasu daga cikin Fulani da Hausawa suka fara ficewa daga jihar Enugu, inda aka samu rikici na baya-bayan nan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.