Isa ga babban shafi
Najeriya

NUPENG da PENGASSAN na adawa da matakin raba NNPC

Kungiyoyin ma’aikatan man fetir a Najeriya wato NUPENG da PENGASSAN sun yi watsi da shirin rarraba babban kamfanin mai na NNPC zuwa rassa har 30, saboda fargaba  cewar ma’aikata da dama a kamfanin zasu rasa ayyukansu.  

Motar dakon man kanfanin NNPC.
Motar dakon man kanfanin NNPC. Getty Images/Suzanne Plunkett
Talla

A ranar Laraba ne dai ministan kasa na man fetire Dr Ibe Kachikwu ya bayyana matakin kasa kamfanin NNPC har rassa 30.

Kuma ministan yace nan da mako guda ne suke fatar aiwatar da sauyin a kamfanin na NNPC.

Amma shugaban kungiyar PENGASSAN ta manyan ma’aikatan mai a Najeriya ya ce ba su goyon bayan matakin na raba NNPC, a cewar shugaban kungiyar Emmanuel Ojugbana a yanke shawarar raba NNPC ne ba tare da saninsu ba.

Sai dai yace  zasu gana domin daukar matakin da ya dace don suna son asan yadda matakin zai shafi ma’aikata.

Tun bayan hawan shugaba Muhammadu Buhari mulki ne ake ta duba batun sake fasalta kamfanin NNPC dake fama da matsalar rashawa.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.