Majalisar Dattawan Najeriya ta fara tantance sunayen ministocin gwamnatin Buhari
A yau Talata ake saran wakilan majalisar Dattawan Nigeria su koma zaman su a Abuja domin fara muhawara gameda jerin sunayen da Shugaba Muhammadu Buhari ya aika masu na mutanen da zai na da a kan mukaman Ministoci.
Wallafawa ranar:
Tun a makon jiya aka gabatar wa majalisar dattawan sunayen sabin ministocin da shugaba Buhari ke son nadawa a kan mukaman ministocin
Shugaban majalisar Dattawan Bukola Saraki ya ce zasu gaggauta muhawara domin shugaban kasar ya sami ayarin wadanda zasu taya shi gudanar da ayyukan da Gwamnatin ta sagaba.
An dai jima a na dakon sabin ministocin na gwamnatin Buhari ta Farko tun bayan karbe shugabancin kasar da ya yi daga hannun tsohon shugaban kasar Good luck Jonathan da ake zargin gwamnatinsa, da zama ummal haba’isa sukurkutarda lamurra a kasar ta Najeriya
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu