Isa ga babban shafi
Saudi-Najeriya

Alhazan Najeriya da suka mutu a Saudiya sun karu

Hukumar Alhazan Najeriya ta sanar da karin adadin alhazan da suka mutu zuwa 64 sakamakon turmutsitsin da ya auku a Mina wajen Jifan shedan a makon da ya gabata.Kana akwai mutane 244 da ba a san inda suke ba har yanzu.

Gawarwakin Alhazan da suka rasu a turmutsitsin aikin Hajji
Gawarwakin Alhazan da suka rasu a turmutsitsin aikin Hajji REUTERS/StringerTEMPLATE OUT
Talla

Kakakin hukumar Malam Uba Mana wanda ya bada Sanarwa a garin Makkah na kasar Saudiya ya ce izuwa yanzu bayan wadanda suka mutu akwai wasu 71 da ke kwance a Asibiti sakamakon raunin da suka samu

Shima dai Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya nemi Hukumar Alhazan kasar ta tabbatar da cewa lallai an san halin da dukkan alhazai suke ciki.

Umarni Buhari ya biyo bayan rashi gamsassun bayanai ne daga hukumomin Najeriya game da mamata.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.