Zaben Najeriya nasara ce ga Afrika
Majalisar Dinkin Duniya tace nasarar da aka samu a zabukan Najeriya zai bayar da damar gudanar da zabubbuka masu inganci a Yankin Afirka ta Yamma. Jakadan Majalisar a Yankin, Muhammad ibn Chambers ne ya bayyana haka bayan kammala zaben gwamnoni cikin kwanciyar hankali.
Wallafawa ranar:
Chambers ya ce hukumar zaben Najeriya ta taka rawar gani, musamman ganin irin matsin lambar da ta samu daga al’ummar kasar da kuma masu sa ido daga kasashen duniya wajen ganin an yi zabe mai inganci.
Chambers wanda ya yabawa shugaban Najeriya mai barin gado Goodluck Jonathan kan rawar da ya taka wajen amincewa da sakamakon zaben, ya ce yana da fata mai kyau cewar za a samu zabubbuka masu inganci a kasahsen Togo da Guinea da Cote d’Ivoire da Burkina Faso a cikin wannan shekarar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu