Isa ga babban shafi
EU-Najeriya

Tawagar Turai za ta ci gaba da sa ido a Najeriya

Tawagar masu sa ido na Kungiyar Tarayyar Turai ta ce za su ci gaba da zama a Najeriya har lokacin da za a gudanar da babban zabe a kasar. Kungiyar Kasashen Turai tace ta dauki zaben shugaban kasar Najeriya da za a yi a watan gobe da matukar muhimmanci saboda kimar kasar da farin jininta a duniya da kuma karfin tattalin arzikinta a Afirka.

Tawagar masu sa ido na kungiyar Tarayyar Turai a zaben Najeriya
Tawagar masu sa ido na kungiyar Tarayyar Turai a zaben Najeriya scannewsnigeria.com
Talla

Shugaban tawagar masu sa ido na kungiyar Santiago Fisas ne ya bayyana haka lokacin da ya ziyarci Gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso.

Jami'in ya ce zaben Najeriya na da matukar muhimmanci ga Afirka da kungiyar kasashen Turai.

Tawagar wakilan na Turai dai sun iso Najeriya tun kafin Jam'iyyun siyasa su yi taron zaben fidda gwani a tsakaninsu, kuma babban Jami’in na Turai ya ce suna nan suna ci gaba da sa ido kan abin da ke faruwa a Najeriya

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.