Dambarwar siyasar Jihar Taraba bayan dawowar Gwamna Dan Baba Suntai
Wallafawa ranar:
Kunna - 21:21
A watan Oktoban bara ne Gwamnan Jihar Taraba, Dan Baba Suntai ya samu hadarin jirgi, lamarin da ya sa ya fita kasar waje domin neman magani, wanda hakan ya sa aka ba mataimakinshi Alhaji Garba Umar damar tafiyar da ragamar mulkin Jihar. A kuma farkon makon da ya gabata ne, Gwamna Suntai ya dawo daga jinya, lamarin da har ila yau ya haifar da kace - nace a daukacin Najeriya yayin da Suntai ya yi yunkurin ci gaba da aiki. To sai dai Majalisar Dokokin Jihar, wacce ta ziyarci gwamnan ta dakile wannan yunkuri na shi ta na mai cewa bai samu cikakkiyar lafiyar da za a mayar mai da ragamar tafiyar da mulkin jihar ba. Akan wannan batu shirin Duniyramu A Yau ya tattauna.