Wani rahoton kungiyar Transparency International yace an samu karuwar cin hanci a shekaru biyu da suka gabata, wanda ya karya farin jinin mahukunta ga al’ummar duniya musamman bangaren sharia’a da ‘Yan siyasa da kuma ‘Yan sanda. Cikin jerin sahun kasashe 10 da matsalar cin hanci da rashawa ta yi kamari, 8 daga cikinsu, kasashen Afrika ne, a cewar kakakin kungiyar Transparency. Bashir Ibrahim Idiris ya tattauna da abokokan shirinsa game da rahoton