Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Bauchi ta kafa kwamitin sasanta rikicin Tafawa Balewa a Najeriya

A Najeriya mako daya bayan canja mazaunin karamar hukumar Tafawa Balewa, zuwa garin Bununu, gwamnatin Jahar Bauchi ta bullo da wani zauren tuntuba da yafewa juna tsakanin kabilun da ke fafatawa da juna a wannan yanki.

Gidan yarin da 'Yan hursuna 700 suka tsere a Jahar Bauchi Tarayyar Najeriya
Gidan yarin da 'Yan hursuna 700 suka tsere a Jahar Bauchi Tarayyar Najeriya AFP/Aminu ABUBAKAR
Talla

03:41

Rehoton Shehu Saulawa Daga Bauchi

Shehu Saulawa

Mai Martaba Sarkin Bachi Alh. Rilwanu Sulaiman Adamu wanda shi ne shugaban zauren muhawarar yace babban aikin da ke gabasu shi ne tattaro bayanai daga kabilun da rikicin ya shafa domin yafewa wa Juna tare da ba gwamnatin Shawara.

An kwashe sama da shekaru 40 ana fafata tsakanin kabilun Fulani da Sayawa kan mallaka amma ana tunanin zauren sasantawar zai shawo kan matsalar tsakanin kabilun biyu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.