Lafiya Jari ce
Kalubalen da ake fuskanta sakamakon karancin likitocin hakora a kasar Nijar
Wallafawa ranar:
Kunna - 09:48
A Jamhuriyar Nijar, kasar da ke da mutane sama da milyan 18 amma kuma take fama da karancin likitocin hakora, yayin da alkalumma ke nuni, duka duka likitocin hakora da ake da su a fadin kasar ba su wuce 50 ba.A kwanakin da suka gabata, Abdoulkarim Ibrahim Shikal wanda ya ziyarci birnin Yamai, ya halarci kaddamar da wani asibitin hakora mai suna Sahhat karkashin jagorancin wata kwararriyar Likita Dr Halima Sule Ummaru, inda masu ruwa da tsaki a harkar lafiyar hakora daga sassan kasar suka halarci wannan biki.