Ilimi Hasken Rayuwa
Makafin da ke sarrafa na'urar komputa a Najeriya (2)
Wallafawa ranar:
Kunna - 10:07
Shirin Ilimi Hasken Rayuwa na wannan makon tare da Abdurrahman Gambo Ahmad ya dora ne kan na makon da ya gabata, in da ya kai ziyara cibiyar horar da makafi ta gwamnatin tarayya a Najeriya don tattaunawa kan ilimi da fasahar da Allah ya hore wa wadannan makafi. Baya ga sarrafa komputa, har ila yau makafin na koyan ayyukan fasahohi da kere-kere da dama a wannan katafariyar cibiya.