Kotu ta yankewa mutane hudu hukuncin kisa a Malaysia
Wata kotun kasar Malaysia, ta yankewa wasu mutane hudu hukuncin kisa, ta hanyar rataya, bayan da ta same su da laifin kashe wata ‘yar kasuwa da abokan huldar ta su uku.
Wallafawa ranar:
Mutanen da suka hada da lauya daya, sun kashe Sosilawati Lawiya, mai shekaru 47, direban ta, lauyan ta da wani ma’aikacin banki a shekarar 2010, lamarin da ya girgiza jama’a, tare da daukar hankulan kafafen yada labarun kasar.
An bayar da sanarwar bacewar mutanen a lokacin da suka je cinikin wani filin lauyan da dan uwan shi a gonarsu.
‘Yan sanda sun ce an kone gawarwakin mutanen, aka kuma zuba burbushin su a kogi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu