Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afrika
Dan wasan Najeriya Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon Afrika na wannan shekarar ta 2023, abin da ya karfafa matsayinsa a jerin manyan 'yan wasa na duniyar tamola.
Wallafawa ranar:
Osimhen wanda ke taka leda a Napoli ya doke Achraf Hakimi na Morocco da Mohamed Salah na Masar wajen lashe kyautar ta gwarzon Afrika.
An gudanar da bikin karrama gwarzon dan wasan na Afrika ne a birnin Marakesh na Morocco, kuma a karon farko kenan tun shekarar 1999 da wani dan wasa daga Najeriya ke lashe kyautar tun bayan Kanu Nwankwo.
A bangaren mata kuwa, Asisat Oshiola ta Najeriya kuma mai taka leda a Barcelona ce ta zama gwarzuwar 'yar wasan Afrika a bana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu