Isa ga babban shafi

Benzema na da 'yancin nuna jimami kan halin da Falasdinawa ke ciki - Lauyansa

Lauyan Karim Benzema ya mayar da martani ga ministan cikin gidan Faransa bayan da ya zargi tauraron kwallon kafar Faransa da alaka da kungiyar 'yan uwa musulmi.

Dan wasan Faransa Karim Benzema
Dan wasan Faransa Karim Benzema REUTERS - HANNAH MCKAY
Talla

Ministan harkokin cikin gida Gerald Darmanin ne ya yi wannan zargin bayan dan wasan da ya lashe kyautar Ballon d’Or kuma tsohon dan wasan gaba na Real Madrid ya wallafa wani sako a shafukan sada zumunta game da goyan bayan Falasdinu a yakin da ake yi tsakanin Isra’ila da Hamas.

Benzema wanda ke taka leda a kungiyar Al Ittihad ta kasar Saudiyya, ya wallafa sakon goyan baya ga Falasdinawa ne ta shafinsa na X.

"Dukkan addu'o'inmu ga mazauna Gaza ne wadanda suka sake fuskantar wadannan hare-haren bama-bamai na rashin adalci, wanda bai ware mata da kananan yara ba."

Darmanin, da yake magana a tashar CNews, ya yi zargin cewa Benzema na da alaka da kungiyar 'yan uwa musulmi".

“Wannan karya ne! Karim Benzema bai taba samun wata dangantaka da wannan kungiyar ba,”in ji Hugues Vigier Lauyan Benzema a cikin wata sanarwa.

Ya ce Benzema kamar da dama daga al’ummar duniya na tausawa Faladinawa ne kan halin da suke ciki, wanda ake alakantawa da laifukan yaki a yankin Gaza, tun bayan harin ranar 7 ga watan Oktoba da Hamas ta kai cikin Isra’ila.

Lauyan ya kara da cewa yana shirin shigar da karar Darmanin kan zargin nasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.