Isa ga babban shafi

Jerin 'yan wasa 30 da za a zabi zakaran Ballon d'Or na bana

An fitar da jerin sunayen ‘yan wasa 30 da za su fafata wajen takarar neman lashe kyautar gwarzon dan wasan shekara ta Ballon d’Or, jerin sunayen da ke fita karon farko cikin shekaru 20 ba tare da sunan tauraron Portugal ba wato Cristiano Ronaldo.

Wannan ne karon farko da ake fitar da wannan jeri ba tare da sunan Cristiano Ronaldo na Portugal ba.
Wannan ne karon farko da ake fitar da wannan jeri ba tare da sunan Cristiano Ronaldo na Portugal ba. © Power Sport Images/Getty Images
Talla

Dan wasan gaba na Najeriya da Napoli Victor Osimhen ya shiga cikin jerin ‘yan wasan da aka zaba a matsayin wadanda za su yi wannan takara ta Ballon d’Or lamarin da ya mayar da shi dan Najeriya na farko da aka zaba domin lashe kyautar bangaren maza tun bayan shekarar 1999. 

Masu shirya kyautar, wato French Football, sun tabbatar da zaben Osimhen ne a daren jiya Laraba, sakamakon rawar ganin da ya taka a kakar wasan da ta wuce, inda ya taimakawa kungiyarsa ta Italiya lashe kyautar Scudetto ta farko cikin shekaru 33. 

Osimhen ya zura kwallaye 25 a gasar lig a kakar da ta wuce, inda ya doke Lautaro Martinez na Inter Milan da Rafael Leao na AC Milan wajen samun kyautar gwarzon dan wasan gaba a Seria A. 

Ya kuma taimaka wa kungiyar ta kai wasan daf da na kusa da na karshe a gasar cin kofin zakarun nahiyar Turai ta UEFA, kuma ya taka rawar gani wajen taimakawa Super Eagles ta Najeriya samun tikitin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka na wannan shekara da aka jinkirta. 

Wannan matakin ya bai wa dan wasan mai shekaru 24 lambar yabo a matsayin dan Afrika na farko da ya jagoranci jerin 'yan wasan Seria A, yayinda ya goge tarihin George Weah na yawan kwallayen da dan Afirka ya ci a gasar ta Italiya.

'Yan wasa 30 da za su fafata don lashe Ballon d'Or

Julian Alvarez

Nicolo Barella 

Jude Bellingham 

Karim Benzema 

Yassine Bounou 

Kevin De Bruyne 

Ruben Dias 

Ilkay Gundogan 

Antoine Griezmann 

Josko Gvardiol 

Erling Haaland 

Harry Kane 

Khvicha Kvaratskhelia 

Robert Lewandowski 

Randal Kolo Muani 

Emiliano Martinez ne adam wata 

Lautaro Martinez 

Kylian Mbappe 

Lionel Messi 

Kim Min Ka 

Luka Modric 

Jamal Musala 

Martin Odegaard 

Andre Onana 

Victor Osimhen 

Rodri 

Bukayo Saka 

Mohammed Salah 

Bernardo Silva 

Vinicius Jr 

Manchester City ce ta fi kowacce kungiya yawan 'yan wasan da suka shiga wannan jeri, yayinda Afrika ke da wakilcin 'yan wasa 4.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.