Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Ghana na fuskantar barazanar ficewa daga gasar cin kofin Afrika

Ghana na shirin karawa da Comoros yau talata, a karkashin gasar cin kofin Afrika da ke ci gaba da gudana a Kamaru, wasan da ke matsayin babban kalubale ga kasar ta yammacin Afrika domin kuwa matukar ta na son ci gaba da kasancewa cikin gasar dole ta yi nasara a wasan.

Wasan Ghana da Gabon karkashin gasar cin kofin Afrika.
Wasan Ghana da Gabon karkashin gasar cin kofin Afrika. Kenzo Tribouillard AFP
Talla

Yanzu haka tawagar ta Black Stars ke matsayin ta 3 a rukuninta na C bayan samun maki 1 tal a wasanninta 2 da ta doka bayan da ake zura mata kwallon kurarren lokaci a dukkanin karawarta biyu .

Karawar Ghana ta farko dai ta yi rashin nasara hannun Morocco da kwallo 1 mai ban haushi kwallon da aka zura mata a minti na 83 gab da Karkare wasa, yayinda ta tashi wasa kwallo 1 da 1 tsakaninta da gabon shima dai wannan karawa a farko Ghanar ke jagoranci har zuwa minti na 88 gabanin Jim Allevinah na Gabon ya zura mata kwallo mai cike da bajinta.

Da misalin karfe 9 na daren yau wasan zai fara wanda idan har bata yi nasara ba kai tsaye za ta fice daga gasar.  

Morocco dai ke jagorancin rukunin na C da maki 6 bayan nasara a dukkanin wasanninta biyu biye da Gabon mai maki 4 bayan nasara a wasa 1 canjaras a wasa daya, kuma suma dai kasashen biyu wato jagora da mai bi mata Morocco da Gabon kenan nada wasa a yau ko da ya ke ma tuni aka fara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.