Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon Kafa

Liverpool ta kammala wasannin rukuni na tare da rashin nasara ba

Kungiyar kwallon kafa ta Liverpool ta kafa tarihin shiga sahun kungiyoyin da suka kammala wasannin rukuni na gasar cin kofin zakarun Turai ba tare da rashin nasara ko da a wasa guda ba, bayan nasararta kan AC Milan da kwallaye 2 da 1.

Tawagar Liverpool.
Tawagar Liverpool. MIGUEL MEDINA AFP
Talla

Yayin wasan na jiya, wanda zakaran Liverpool Mohamed Salah ya nuna bajinta kwarai, Milan ta fara zura kwallo ta hannun dan wasanta Fikayo Tomori tun a minti na 28 da fara wasa sakamakon kuskuren da mai tsaron ragar Reds Alisson Becker ya yi, amma kuma Mohammed Salah ya farke a minti na 36 kana Origi ya kara guda a minti na 55 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.

Kwallon da Salah ya zura a jiya ta zama kwallo ta 20 cikin wannan kaka kadai daya kunshi 7 karkashin gasar ta cin kofin zakarun turai, wanda ke nuna shi ne dan wasan Liverpool na biyu tun bayan Ian Rush da ya nuna wannan makamanciyar bajinta.

A bangare guda shi ma Origi kwallon tasa ta jiya ita ce ta farko da dan wasan ya zurawa kungiyar tasa tun bayan ta wasan karshe na makamanciyar gasar a 2019 lokacin da Liverpool ta doke Tottenham tare da dage kofin gasar.

Liverpool dai za ta shiga rukunin ‘yan 16 na gasar a jerin kungiyoyin da za a fi jin tsoron haduwa da su, ko da ya ke babbar barazanar da za ta fuskanta bai wuce daga takwarorinta kungiyoyin firimiya da suka kunshi Manchester City da Chelsea ba, sai kuma Real Madrid ta Spain da Bayern Munich wadanda dukkaninsu sun nuna bajinta a matakin na rukuni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.