Kamfanin Najeriya ya fara daukar nauyin gasar Kenya
Kamfanin cacar yanar gizo na Najeriya Betking ya zama sabon mai daukar nauyin gasar firimiya lig ta kasar Kenya a karkashin wata hadaka ta zunzurutun kudi har Dala miliyan 11.
Wallafawa ranar:
Wannan hadakar za ta ci gaba da aiki har zuwa shekarar 2025 kamar yadda Hukumar Kwallon Kafar Kenya ta sanar a wannan Alhamis.
Hukumar ta ce, sabon daukar nauyin shi ne mafi girma da aka gani a tarihin kwallon kafa a kasar ta Kenya.
A karkashin hadakar, za a rika biyan kowane klub da ke taka leda a gasar lig din ta Kenya akalla Shilling miliyan 8 a kowacce shekara.
Wannan na zuwa ne a bayan kamfanin SportPesa ya janye daga daukar nauyin gasar ta Kenya a cikin watan Satumba sakamakon rikicin kudin haraji tsakaninsa da gwamnatin kasar.
Betking ya tsallaka zuwa Kenya ne a daidai lokacin da gasar firimiyar Najeriya ke fuskantar matsaloli da dama, ciki har da batun daukar nauyi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu