Isa ga babban shafi
Wasanni

Milan ta shiga jerin kungiyoyin Turai masu zawarcin Osimhen

AC Milan ta shiga sahun kungiyoyin kwallon kafar dake neman kulla yarjejeniyar da dan wasan gaba na Najeriya dake kungiyar Lille a Faransa Victor Osimhen.

Wasan Najeriya dake kungiyar Lille a Faransa, Victor Osimhen.
Wasan Najeriya dake kungiyar Lille a Faransa, Victor Osimhen. AFP
Talla

Sai dai duk da bayanai sun ce Milan na shirin gabatar da tayi mai romo ga dan wasan, har yanzu takwararta a gasar Seria A wato kungiyar Napoli aka fi sa ran za ta samu nasarar daukar Osimhen mai shekaru 21.

A baya baya nan dan wasan da kungiyarsa ta Lille ke neman euro miliyan 60 kafin saida shi, yayi tattaki zuwa Italiya, inda ya gana da shugabannin kungiyar Napoli.

A yanzu haka dai, Osimhen na cikin matasan da suka yi fice a nahiyar Turai kan tamaula, wanda a kakar wasa ta bara ya ci wa Lille kwallaye 18 daga cikin wasanni 38 da ya buga mata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.