Yarima Ali na Jordan zai tsaya takarar shugabancin FIFA
Yarima Ali bin Hussain na Jordan ya bayyana sabuwar aniyarsa ta neman kujerar shugabancin hukumar kwallon kafa ta duniya wadda a yanzu ke karkashin jagorancin Sepp Blatter.
Wallafawa ranar:
Yarima Ali ya ce shi kadai ne zai iya tinkarar matsalar cin hancin da rashawa da suka addabi hukumar ta FIFA tare da magance ta.
A watan Mayun da ya gabata Yarima Ali ya kalubalanci Sepp Blatter a zaben da aka gudanar, to sai dai gabanin kammala zaben ne ya janye, kuma daga bisani Blatter ya lashe zaben.
To sai dai a yanzu Yariman yana bukatar ya kammala abinda ya fara a farko na Kalubalantan Blatter kamar yadda ya shaidawa magoya bayansa a yau laraba da suka hada da Firai Ministan Kasar Jordan Abdullah Nsur.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu