Zidane da Ronaldo sun jagoranci wasan Ebola
Tsoffin ‘yan wasan kwallon duniya Zinedine Zidane da Ronaldo na Brazil sun jagoranci wani wasan yaki da Talauci karo na 12 a jiya Litinin a filin wasa na kungiyar Saint-Etienne a Faransa. An gudanar da wasan ne na musamman domin yaki da cutar Ebola tare da samar da kudaden tallafi ga kasashen yammacin Afrika guda uku inda cutar ta fi yin kisa.
Wallafawa ranar:
Zidane daRonaldo jekadu ne na musamman ga hukumar samar da ayyukan ci gaba ta Majalisar Dinkin Duniya.
Daga cikin tsoffin ‘yan wasan da suka rufe wa su Zidane da Ronaldo baya akwai, Fabien Barthez da Eric Abidal da Clarence Seedorf da David Trezeguet da Jay-Jay Okocha na Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu