Okocha ya koka da gazawar Keshi a wasan Najeriya da Iran
Tsohon dan wasan Najeriyar Jay Jay Okocha ya nuna alhininsa kan yadda Najeriya ta yi kasa a gwiwa a wasanta da Iran a gasar cin kofin wasan kwallon kafa na duniya, inda ya ce wannan dama da Najeriya ta zubar, kamata ya yi a ce ta samu nasara.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Hasali ma Okocha ya dora laifin wannan rashin nasara akan mai horar da ‘yan wasan Stephen Keshi, inda ya kara da cewa bai dauki lokaci wajen horas da ‘yan wasan a fannin basirar buga wasa ba.
Okocha ya kuma soki Keshi kan yadda ya canja dan wasansa Victor Moses a zagaye na biyu inda ya sako shola Ameoba.
Najeriya za ta kara da kasar Bosnia ne a wasanta na gaba, wasan da zai zamanto dole Najeriyar ta lashe muddin ta na so ta tabuka wani abu a gasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu