FA: An hada City da Chelsea, Arsenal da Liverpool
An hada manyan kungiyoyin kwallon kafa su kashe kansu a zagaye na biyar a gasar FA ta Ingila a jiya lahad Inda aka hada Chelsea wasa da Manchester City kungiyoyin da ke harin lashe kofin Premier a bana.
Wallafawa ranar:
A daya bangaren kuma an Hada Arsenal da ke jagorancin Teburin Premier wasa da Liverpool a zagaye na biyar inda za’a tantance ‘Yan wasa 8 da zasu tsallake zuwa zagayen Kwata Fainal.
A tsakiyar watan gobe mai kamawa ne za’a yi wannan fafatawar tsakanin manyan kungiyoyin guda hudu.
A watan Nuwamba, Arsenal ta doke Liverpool ci 2-0 kuma kungiyoin biyu zasu fara kece raini a Anfield ne a league kafin makon da zasu sake fafatawa a FA a filin wasa na Emirates.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu