An hada PSG wasa da Saint-Etienne a Faransa
An hada kungiyoyin da zasu kara da juna a zagaye na biyu a gasar neman lashe kofin kasar Faransa. Kuma akwai barazana ga PSG domin zata kara ne da Saint-Etienne da ke rike da kofin gasar. A bara, PSG ta sha kashi ne a hannun Saint-Etienne a wasan dab dana karshe.
Wallafawa ranar:
Kungiyar Lyon zata kara ne da Reims, Nantes kuma ta kece raini daAuxerre.
An hada Marseille da Toulouse, Evian da Bastia, Rennes da Bordeaux.
A daya bangaren kuma Kocin Faransa ya kira dan wasan Manchester United Patrice Evra cikin tawagar ‘Yan wasa 24 da za su fafata da Ukraine a wasan neman tsallakewa zuwa gasar cin kofin Duniya a Brazil.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu