Goerge Weah zai jagoranci wasan tawagar tsoffin ‘Yan wasan Afrika a Liberia
Tsohon fitacce dan wasan Liberia George Weah zai jagoranci wani wasa na musamman da ya kunshi tsoffin zaratan ‘yan wasan Afrika domin tabbatar da zaman lafiya da sasantawa a kasar shi saboda yakin basasa da ya janyo hasarar rayukan mutane kimanin 250,000.
Wallafawa ranar:
Goarge Weah wanda gwamnatin Liberia ta zabe shi a mastayin jekadan wanzar da zaman lafiya a kasar. ya gayyaci tawagar ‘yan wasa da suka hada da manyan tsoffin ‘yan wasan Kamaru guda biyu Roger Milla da Patrick Mboma, da JJ Okocha na Najeriya.
A ranar Assabar ne dai ake sa ran tsoffin ‘Yan wasan za su tara dimbin masoya a filin wasa da ke birnin Monrovia.
Goarge Weah ya taba lashe kyautar gwarzon dan wasan Turai a shekarar 1995.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu