PSG na burin Ibrahimovic ya maimaita bajintarsa akan Rennes
Club din Paris Saint Germain dake kasar Faransa na saka ido akan dan wasanta, Zlatan Ibrahimovic, inda suke sa ran zai maimaita irin bajintar da ya nuna a wasan sada zumunci da kasarsa ta Sweden ta buga da kasar Ingila inda ya zira kwallaye hudu shi kadai.
Wallafawa ranar:
A gobe Asabar ne dai PSG zata kara da club din Rennes a gasar French Ligue, inda a karshen satin da ya gabata ne PSG ta yayi kunnen doki da club din da Monteplier wacce ita ke rike da kofin gasar.
A shekaran jiya ne kasar Sweden ta lallasa kasar Ingila da ci 4-1 a wasannin da aka buga na sada zumunci a wurare daban-daban a duniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu