Isa ga babban shafi
Tennis

Djokovic zai fara haskawa a gasar Roland Garros

A yau litinin ne aka shiga kwana na biyu a gasar Tennis ta Roland Garros a Faransa. A yau ne kuma Novak Djokovic zai fara haskawa a gasar inda zai kara da Potito Starace dan kasar Italia a zagayen Farko.

Novak Djokovic da Rafael Nadal da Roger Federer wadanda ake hasashen zasu iya lashe gasar French Open ta Roland Garros
Novak Djokovic da Rafael Nadal da Roger Federer wadanda ake hasashen zasu iya lashe gasar French Open ta Roland Garros Reuters/Montage RFI
Talla

Novak Djokovic dai ya lashe kofin Wimbledon da US Open da Australian Open amma bai taba buga wasan karshe ba a French Open. Domin sau uku yana shan kashi a zagayen kusa da karshe.

Roger Federer kuma wanda ya taba lashe Roland Garros a shekarar 2009, a yau Litinin ne, shi ma zai fara haskawa inda zai kara da Tobias Kamke dan kasar Jamus.

A fafatawar farko a jiya Lahadi Jo-Wilfried Tsonga na Faransa ya samu nasarar doke Andrey Kuznetsov na Rasha.

A bangaren mata kuma, mai rike da kofin gasar Li Na ‘Yar kasar China a yau zata kece raini da Sorana ‘yar kasar Romania.

Victoria Azarenka kuma jarumar Tennis a Duniya zata kara ne da Alberta Brianti ‘yar kasar Italia.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.