A daidai lokacin da ake shirye-shiryen zaben shugaban kasa na 'yan Majalisa a watan fabarairun 2016, hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun cafke tsohon shugaban Majalisar Dokokin kasar Hama Amadou wanda ake zargi da fataucin jarirai daga Najeriya, yayin da a jihar Kebbi da ke Tarayyar Najeriya, jam'iyyar PDP ke neman a tube gwamna Atiku Bagudu, saboda a cewar jam'iyyar, gwamnan mai laifi ne kafin zaben sa.Wadannan batutuwa ne shirin na wannan mako ya mayar da hankali a kai tare da Bashir Ibrahim Idris.