Ana ci gaba da cece-kuce kan hukuncin zabe a Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 16:26
A Najeriya ana ta cece-ku ce a game da samun takardun kotun daukaka kara wadanda ke kunshe da abin da ya sha bambam da hukuncin da alkalan kotun suka yanke, wanda ya jaddada soke zaben gwamnan jihar Kano da kotun sauraron korafe-korafen zabe ta yi tun da farko.
Wannan na zuwa ne jim kadan bayan da tsohon shugaban kasar, Olusegun Obasanjo ya ce irin tsarin mulkin dimokaradiyyar da kasashen Afrika suka dauko daga kasashen yamma bai dace da Najeriya da ma sauran kasashen nahiyar ba, saboda babu abin da ya tsinana musu.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakken shirin tare da Usman Tunau.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu