Ra'ayoyin Masu Saurare kan kudin diyyar bautar da 'yan Afrika
Wallafawa ranar:
Kunna - 16:43
Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya bukaci hadin gwiwa da saura takwarorinsa na Afirka domin ganin an tilasta wa ‘yan mulkin mallaka biyan diyya saboda yadda suka rika dibar mutane domin bautar da su daga Afirka.
Shugaba Akufo-Addo wanda ke jawabi a gaban takwarorinsa na Afirka da kuma yankin Caribean a birnin Accra, ya ce an kwashe dubban majiya karfi domin bautar da su, lamarin da ya taimaka wajen talauta nahiyar.
Shin me za ku ce a game da wannan yunkuri da shugaban na Ghana ya bijiro da shi?
Anya abu ne mai yiwuwa a samu biyan bukata daga tsoffin ‘yan mulkin mallakar?
Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayyoyin jama'a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu