Ra'ayoyin Masu Saurare kan kisan gillar da aka yi wa mutane a Kamaru
Wallafawa ranar:
Kunna - 16:41
Mahukunta a Kamaru, sun ce mutane 25 ne ‘yan bindiga suka yi wa kisan gilla a cikin yanayi na tozartarwa, lura da cewa wasu daga cikin mutanen an kashe su ne bayan an yi musu fyade tare da nuna hotunansu a hoton bidiyo.
Wannan dai ya wakkana ne a daya daga cikin yankunan da masu amfani da turancin Ingilishi ke fafutukar ballewarsu daga kasar ta Kamaru.
Shin me za ku ce a game da yadda ‘yan bindigar suka karkata akalar hare-harensu ga fararen hula bayan tsawon shekaru suna afka wa jami’an tsaro?
Shin ko yaya ya kamata a tunkari wannan matsala ta ‘yan aware da ke ci gaba da raba kawunan al’umma a Kamaru?
Ku latsa alamar sauti domin sauraren mabanbantan ra'ayoyin jama'a kan wannan maudu'in.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu