Sanata Abdulaziz Yari kan shugabancin majalisun dokokin Najeriya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:53
Kokarin Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu na ganin sabbin zababbun ‘yan majalisun tarayya sun amince da zabin da aka musu na shugabannin da zasu jagorance su a majalisa ta 10 na ci gaba da fuskantar tirjiya daga wani bangare na ‘yan majalisun da kuma kungiyoyi daban daban a sassan Najeriya.
Rahotanni sun ce kungiyoyin kare hakkokin dimokiradiya da na ‘yan arewacin kasar na bukatar ganin an baiwa ‘yan majalisun damar zabin shugabannin su, maimakon yi musu dauki dora, wanda suka ce zai mayar da majalisar tamkar ‘yar ashin shata.
Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da daya daga cikin wadanda suka bijirewa matsayin jam’iyyar APC wajen shiga takarar shugabancin majalisar, wato Sanata Abdulaziz Yari.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu