Janar Sani Usman Kukasheka kan cika shekaru 75 da fara aikin wanzar da zaman lafiya
Wallafawa ranar:
Majalisar Dinkin Duniya ta ce dakarun samar da zaman lafiya sama da 4,200 suka rasa rayukansu a cikin shekaru 75 da akayi ana tura su yankunan da ake samun tashin hankali domin wanzar da zaman lafiya.
Sakatare Janar na Majalisar Antonio Guterres ya bayyana haka lokacin da yake jinjinawa sojoji daga kasashe 125 da suka sadaukar da rayukansu tun daga shekarar 1948 da aka fara tura su kasashen da ake fama da tashin hankali 71.
Dangane da wannan, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Janar Sani Usman Kukasheka mai ritaya Wanda yayi aikin samar da zaman lafiya a kasashen Saliyo da Habasha da kuma Eritrea.
Ga yadda zantawarsu ta gudana.
Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar............
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu