Kamar dai sauran kasashe na duniya, yanzu haka Najeriya na ci gaba da kokarin ganin ta kwaso ‘yan asalin kasar daga Sudan zuwa gida, lura da yadda lamarin tsaro ke dada tabarbarewa.
Yanzu haka shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa a Najeriya wato NEMA Mustapha Habib Ahmed yana kasar Masar don tsara yadda za’a fara kwaso ‘yan kasar daga wani yanki da ke kan iyakar Masar da Sudan.
To domin jin inda aka kwana, wakilinmu na Abuja Mohammed Sani Abubakar ya zanta da shugaban hukumar ta Nema.
Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu