Adamu Rugu-rugu, tsohon kwamandan Boko Haram ne da ya tuba tare da mika wuya domin ci gaba da rayuwa tsakanin al'ummar jihar Borno ta Najeriya. Ya shaida wa RFI Hausa cewa, lallai sun shiga cikin kungiyar ce bayan an yaudare su da sunan adddini, amma yanzu sun gane gaskiya kuma har ga Allah sun yi nadamar barnar da suka yi.
Rugu-rugu ya ce, babu abin da ke tayar masa da hankali a lokacin da suke rayuwa a dajin Sambisa kamar yadda jiragen sojin saman Najeriya ke yi musu barin-wuta, yana mai cewa, kimanin mayakan 200 zuwa 300 ne ke mutuwa a duk lokacin da sojoji suka kaddamar musu da hare-haren sama.
Ku latsa alamar sauti domin sauraren cikakkiyaar hirarsa da wakilinmu Bilyaminu Yusuf.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu