Ibrahim Dosara kan dokar gwamnatin Zamfara na takaita zirga-zirgar mutane
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:24
Gwamnatin jihar Zamfara dake Najeriya ta sanar da kafa dokar hana fita a wasu garuruwa da kananan hukumomin dake jihar saboda karuwar hare haren 'yan ta’adda.
Gwamnatin ta kuma sanar da dakatar da tarurrukan siyasa har zuwa illa masha Allahu da kuma rufe wasu kasuwanni da hanyoyin mota saboda baiwa jami’an tsaro damar tunkarar 'yan ta’adda a samamen da zasu kaddamar.
Dangane da daukar wadannan tsauraran matakai Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da kwamishinan yada labarai na jihar ta Zamfara, Ibrahim Dosara.
Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu