Ya Tabbata cewar shugabannin kasashen ECOWAS zasu gudanar da wani taro na musamman a New York, inda ake gudanar da taron Babban Zauren Majalisar Dinkin Duniya na 77 a wannan mako.
Daga cikin batutuwan da taron ECOWAS zai duba harda batun sojojin Cote d’Ivoire 46 dake tsare a Mali tun daga ranar 10 ga watan Yuli.
Ministan harkokin wajen Najeriya, Geoffrey Onyeama ya amsa wasu tambayoyi dangane da taron daga abokan aikinmu na Sashen Faransaci Christophe Boisbouvier da Marc Perelman na tashar France 24 a birnin New York.
Latsa alamar sauti domin sauraron fassarar jawabin nasa
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu