Isa ga babban shafi
Bakonmu a Yau

Aliyu Dawobe kan ranar bikin tunawa da mutanen da suka bata a duniya

Wallafawa ranar:

Majalisar Dinkin Duniya ta ware ranar 31 ga watan Agustan kowacce shekara a matsayin ranar da ake mayar da hankali akan mutanen da suka bata, inda kungiyar agaji ta ICRC tace a nahiyar Afirka kawai ana da mutane dubu 64 da suka bata.

Majalisar dinkin duniya na bikin wannan rana ne domin nemo mafita ga mutanen da ke cikin wannan matsala
Majalisar dinkin duniya na bikin wannan rana ne domin nemo mafita ga mutanen da ke cikin wannan matsala AP - Shafiqur Rahman
Talla

Alkaluman kungiyar sun bayyana cewar a Najeriya kawai akwai mutane sama da dubu 25 da suka bata, kuma kusan dubu 14 daga cikin su yara ne kanana.

Dangane da bikin irin wannan rana, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan yada labaran kungiyar ICRC a Najeriya, Aliyu Dawobe.

Latsa alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Sauran kashi-kashi
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.