Tafiya cin rani kasashen Turai da Yan Afirka keyi wanda ke tattare da hadari sannu a hankali na neman zama ruwan dare musamman a kasashen dake yankin Afirka ta Yamma, duk da hadarin dake tattare da shi.
Fatima Mustapha, kwarariyar Yar Jarida a Ghana ta gudanar da bincike,al'amarin da ya kai ta ga gabatar da shiri na musamman wanda yayi dubi dangane da hadarin dake tattare da wannan tafiya da kuma irin halin da wasu daga cikin matafiyan ke samun kan su.
Ga abinda ta shaidawa wakilinmu a Ghana Abdallah Shamun Bako game da binciken da tayi akai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu