Bakonmu a Yau
Tattaunawa da Alhaji Muhammadu Magaji kan taimakon bankin AfDB ga manoman Afrika
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:57
Bankin raya kasashen Afirka AfDB ya ware dala biliyan guda da rabi don agajin gaggawa ga jama’ar da ke nahiyar wajen shawo kan matsalar karancin abinci sakamakon yakin kasar Ukraine. Shugaban Bankin Akinwumi Adeshina ya ce akalla manoma miliyan 20 a Afirka za su amfana da shirin don noma tan miliyan 30 na nau'in abinci iri iri galibi wadanda ake sayowa daga Ukraine. Kan hakan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Sakataren yada labaran kungiyar manoman Najeriya Alhaji Muhammadu Magaji.