Tattaunawa da Farfesa Isa Marte kan lambar yabo da aka baiwa Zulum
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:20
Gwamnan Jihar Borno dake Najeriya, Farfesa Babagana Zulum ya samu lambar yabo da jaridar The Sun ke bayarwa hazakakkun mutane amatsayin gwarzon gwamnan shakarar 2021 saboda kasancewar sa jajirtaccen shugaba a cikin lokaci mafi tsanani.
Yayin katsaitaccen bukin da aka gudanar a Eko Hotel dake birnin Lagos a karshen mako Zulum da wasu hazakukun mutane da suka hada da ‘yan siyasa da ‘yan kasuwa sun karbi lambar yabo da Jaridar The Sun ke bayarwa duk shekara, cikinsu harda Shugaban Majalaisar dattawa Ahmad Lawan da gwamnan Bauchi Bala Mohammed da na Imo da sauransu.
Wannan na zuwa ne kwanaki bayan ziyarar Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres zuwa Maiduguri inda ya yabawa gwamnatin jihar akan matakan da take dauka.
Bayan kammala bikin karrama Zulum a Lagos, Ahmed Abba tattauna da Farfesa Isa Marte Hussein, shugaban ma’aikatan fadar gwamnatin Jihar Borno wanda ya wakilci Zulum, kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu