Bakonmu a Yau
Dr Yahuza Getso kan sako mutum na farko cikin fasinjan jirgin kasan Abuja
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:01
Sakamakon sako mutum na farko daga cikin jerin fasinjojin da akayi garkuwa da su a harin da aka kai wa jirgin kasan da ya taso daga Abuja zuwa Kaduna, a cikin wani faifan bidiyo da ‘yan bindigar suka fitar, suka ce ba sa sha’awar a biya su kudi, sai dai gwamnati ta biya musu bukatun da suke nema, duk da ya ke akwai rahotanni da ke nuna saida aka biya wasu kudi kafin sako shi. Dr Yahuza Getso masani a bangaren tsaro kuma kwararre wajen tattara bayanan sirri, ya yi mana sharhi game da wannan batu.