Buhari ya bada umurnin shirin farfado da gandun daji don makiyaya
Wallafawa ranar:
Kunna - 03:42
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bada umurnin fara Nazari akan gandun dajin kiwon makiyaya 368 dake Jihohin kasar da zummar farfado da su domin magance rikicin da ake samu tsakanin manoma da makiyaya.Mai Magana da yawun shugaban Garba Shehu yace Buhari ya dauki matakin ne sakamakon shawarar kwamitin da Babban Hafsa a fadar sa Farfesa Ibrahim Gambari ya gabatar masa.
Dangane da wannan mataki Bashir Ibrahim Idris ya zanta da Sakataren Kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah, Baba Usman Ngelzerma kuma ga yadda zantawar su ta gudana.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu